Ci gaba da fid da sakamakon zaɓe a Nijar
January 13, 2011Talla
Kwanaki biyu bayan kammala zaɓukan ƙananan hukumomi da gundumomi a Janhuriyar Nijar ana ci gaba da fitar da sakamakon zaɓukan. To sai dai kuma ba dukkan 'yan ƙasar ne suka gamsu da yadda al'amura suka wakana ba, inda wasu ke ƙorafin cewar zaɓen dai ya bar ƙura a baya, musamman ma ta la'akari da jinkirin da aka samu a wasu yankuna sakamakon rashin isasshen kayan aiki da kazalika da ma wasu 'yan takarar dake iƙirarin cewar ba a gabatar da ainihin takardunsu na zaɓe a rumfunan zaɓukan ba. Domin ji ƙari ga rahotanninmu daga Salissou Kaka a Maraɗi da Tila Amadou daga Agadez can ƙasa.
Mawallafa: Salissou Kaka/Tila Amadou
Edita: Ahmad Tijani Lawal