SiyasaAsiya
Bangladesh ta tsayar da lokacin gudanar da babban zabenta
August 5, 2025Talla
Shugaban gwamnatin rikon kwarya na BangladeshMuhammad Yunus, ya ayyana watan Fabarairun shekarar 2026 mai kamawa a matsayin lokacin gudanar da babban zaben kasar.
Wannan na cikin jawabin da shugaban ya gabatar ranar Talata, ta gidan talabijin din kasar, bayan cika shekara guda da hambarar da tsohuwar firaministar kasar Sheikh Hasina, wadda ta tsere zuwa Indiya a ranar 5 ga Agustan 2024, sakamakon zanga-zangar juyin-juya halin da ta yi awon gaba da kujerarta.
Karin bayani:MDD: Tsohuwar gwamnatin Bangladesh ta murkushe masu bore 1,400
Mr Yunus ya alkawarta shirya ingantaccen zabe karbabbe ga kowa cikin gaskiya da adalci.