An ayyana tsagaita wuta a rikicin yankin kudancin Siriya
July 15, 2025Talla
Fadan dai ya barke ne da safiyar jiya, yayin da sojoji suka kutsa cikin birnin da ke kudancin kasar, wanda ke karkashin ikon bangarori daban daban na Druze .
Arangaman ya biyo bayan kalamai masu cin karo da juna daga shugabannin addinai na garin, wadanda galibi suka bukaci mayakan da su ajiye makamansu.
Ministan tsaron Siriya Murhaf Abu Qasra a kan shafinsa na X, ya ayyana tsagaita wuta ga dukkan sassan da ke fada a cikin birnin Sweida, bayan yarjejeniya da manyan jami'an birnin.